2024-05-13 08:40:21
ZIKIRIN SAFE DA MARAICE
حَسْبِيَ اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ عَلَيْهِ تَوَكَّلْتُ وَهُوَ رَبُّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ. (سبع مَرّات)
Hasbiyal-lahu la ilaha illa huwa, 'alayhi tawakkalt, wahuwa rabbul-'arshil-'azeem (7)
Allah ya ishe ni, babu abin bautawa da gaskiya sai Shi. A gare Shi kadai na dogara, shi ne Ubangijin al'arshi mai girma (sau bakwai da safe da maraice).
Wanda ya karanta ta kamar yadda aka ce, Allah zai yaye masa duk abin da ya dame shi na al'amarin duniya da na lahira.
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk musulmin da ya karanta wannan addu’ar sau bakwai da safe, sau bakwai da yamma, to Allah zai azurta shi da abin da ya isar masa da dukkan damuwarsa.
Muna sane da cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Shi, don haka mu fayyace dalilin da ya sa ya ishe mu, kamar yadda ya mallaki sifofin da suka sanya shi ya cancanci a bauta masa.
Kamar yadda Allah ya isar mana, bangaren addu’a na gaba shi ne bayyanar da sanin haka, wato mu dogara gareshi shi kadai wato muna da Tawakkul gareshi.
Domin mu kara tabbatar da dalilin da ya sa muka dogara gare shi, muna tunatar da kanmu girmansa, domin shi ne Ubangijin Al'arshi mai girma. An siffanta darajarsa a cikin tafsirin Ayatul Kursiy.
Wannan addu'ar tana tafe ne a kan Tawakkul ga Allah, kuma ita ce kadai daya daga cikin addu'o'in da za a yi sau bakwai.
Watakila wannan ya faru ne saboda muhimmancin Tawakkul, da cewa ba abu ne mai sauki ba don haka sai mutum ya yawaita addu'a don tabbatar da ma'anoni sun tabbata a cikin zuciyarsa.
A lokacin da Allah ya so ya ambaci manyan halayen muminai a cikin suratu Anfal, sai ya hada da ingancin Tawakkul dinsu a gare shi.
Tawakkul yana kawo fa'idodi masu yawa. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Idan kuna da Tawakku ga Allah yadda ya kamata, da Ya azurta ku kamar yadda Ya azurta tsuntsaye. Shin, ba ka gani ba, da sassafe suke fita da tare da sun mallaka komai ba kuma su koma a koshe a rana?”.
Abu Dawud ya ruwaito hadisi na 5081
Qur'an, Surah Al-Anfal [8:2-4]
Tirmiziy ya ruwaito hadisi na 2344 da Ibnu Majah hadisi na 4164.
Hadisi ya tabbata a cikin Sahihul Bukhari, hadisi na 6472, da Sahih Muslim hadisi na 220.
'Mukhtasar Minhaj Al-Qasideen' na Ibn Qudamah Al-Maqdisi
Hadisi ya tabbata a cikin Sahihul Bukhari, hadisi mai lamba ta: 4563.
5.2K views05:40